Wasanni

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editora: Podcast
  • Duração: 3:59:33
  • Mais informações

Informações:

Sinopse

A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.

Episódios

  • Yadda Ashraf Hakimi ya lashe gwarzon shekara na Afrika karon farko

    24/11/2025 Duração: 09min

    Shirin "Duniyar Wasanni" tare da Khamis Saleh a wannan lokaci zayyi duba ne kan ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafan Afirka da Achraf Hakimi na Morocco ya lashe. A makon daya gabata ne Hukumar Kwallon Ƙafar Afrika CAF, ta bayar da kyautuka ga zaratan ƴan wasan nahiyar da suka nuna bajinta a wannan shekarar da muke bankwana da ita. A yayin bikin da ya gudana a birnin Rabat na ƙasar Morocco, hukumar ta CAF ta sanar da ɗan wasan baya na tawagar ƙasar ta Morocco wanda kuma ya ke yi wa ƙungiyar PSG wasa Achraf Hakimi,  a matsayin wanda ya lashe ƙyautar gwarzon ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Afirka a wannan shekarar. Hakimi ya samu nasarar ce bayan doke shahararrun ƴan wasan nahiyar da suka taɓa lashe kyautar irinsu Mohamed Salah na Masar da ke taka leda a Liverpool,  da kuma Victor Osimhen na Nigeria da ke wasa a Galatasaray. Wannan ne dai karo na farko da ɗan wasan ya taɓa lashe ƙyautar, bayan da a karo biyu a jere ya na ƙarewa a mataki na biyu, a shekarar 2023 da Victor Osimhen ya lashe da kuma 2024 da Ademola Loo

  • Yadda ta kaya a karawar da aka yi tsakanin Najeriya da DR Congo

    17/11/2025 Duração: 10min

    Shirin Duniyar Wasanni a wannan lokaci ya yi duba ne kan yadda wasan ƙarshe na nemon gurbin wakiltar Afrika a matakin duniya, wajen samun tikin zuwa gasar lashe kofin duniya ya gudana tsakanin Najeriya da Jamhuriyar Dimukaraɗiyyar Congo. Karawar da suka yi a filin wasa na Moulay Abdellah da ke birnin Rabat, ta kai matakin dugun daga kai sai mai tsaron gida bayan da suka tashi 1-1.   Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh............

  • Yadda aka fafata a gasar kofin Sardauna ta tsoffin 'yan wasan arewacin Najeriya

    10/11/2025 Duração: 10min

    Shirin Duniyar Wasanni na wannan mako ya mayar da hankali ne kan gasar da tsofaffin ƴan wasan Najeriya da suka fito daga jihohin Arewacin ƙasar suka fafata. A makon daya gabata ne garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, ya karɓi baƙuncin gasar kofin Sardauna karo na 13, wacce tsofaffin ƴan wasan da suka fito daga jihohi 19 na Arewacin Najeriya suka ƙirƙira da zummar sada zumunci da kuma haɗa kan jihohin arewacin ƙasar. Tawagar da ta wakilci jihar Kebbi a wannan gasa ce dai ta yi nasarar lashe wannan kofi, bayan da ta doke takwararta ta Kano a bugun daga kai sai mai tsaron gida da ci 4-3. Latsa alamar sauti don sauraren shirin tare da Khamis Saleh...

  • Karo na biyu a jere Alƙalan wasan Najeriya sun gaza samun wakilci a AFCON

    03/11/2025 Duração: 09min

    Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh a wannan makon ya mayar da hankali kan yadda Najeriya ta gaza samun gurbin alƙalin wasanni a gasar AFCON karo na biyu a jere. A ƙarshen watan da ya gabata ne hukumar ƙwallon ƙafar Afrika CAF ta fitar da jadawalin alƙalan wasanni da za su bayar da gudunmawa a gasar cin kofin ƙasashen Afrika ta AFCON da zata gudana a Morocco cikin watan gobe, amma ba tare da alƙalin wasa ko guda ɗaya daga Najeriya ba. Ko a makamanciyar gasar da ta gabata a Ivory Coast cikin shekarar 2024 babu wakilcin ko da alƙalin wasa guda daga Najeriyar, lamarin da ke matsayin babban koma baya ga wannan ƙasa ta tayi shura a fagen ƙwallo. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin...

página 2 de 2